MDD ta tsawaita takunkumai kan ƙungiyoyin ƴanbindiga a Afirka ta Tsakiya
Majalisar Ɗinkin Duniya ta tsawaita takunkumi kan ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
Majalisar Ɗinkin Duniya ta tsawaita takunkumin da ta ƙaƙabawa ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai da kuma mutanen da ake zargi da kawo cikas ga ƙoƙarin samar da zaman lafiya a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, yayin da rikici ke ci gaba da ta'azzara a ƙasar.
A ƙuri'ar da Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya ya kaɗa a ranar Laraba, an amince da ƙudurin da ya wajabta wa ƙasashe mambobi su ɗauki matakan hana kai ko sayar da makamai da sauran kayan yaƙi ga ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.
Takunkumin, wanda aka tsawaita har zuwa 31 ga Yulin 2027, ya kuma haɗa da haramta wa waɗanda abin ya shafa yin tafiye-tafiye da kuma ƙwace kadarorinsu.
Da yake jawabi a zaman, wakilin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya a Majalisar Ɗinkin Duniya, Marius Aristide Hoja Nzessioué, ya yi maraba da tsawaita takunkumin.
Sai dai ya kuma yi kira ga ƙasashe da su tabbatar da bin matakan takunkumin yadda ya kamata, yana mai nuna takaicinsa cewa har yanzu 'yan tawaye na samun makamai duk da waɗannan matakan.
A lokacin da rikicin cikin gida ya ɓarke a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya a shekarar 2013, Majalisar Ɗinkin Duniya ta kakaba wa ƙasar takunkumin hana shigo da makamai. Tun daga lokacin ake ci gaba da sabunta takunkumin tare da ɗora takamaiman hukunci kan wasu mutane da ake dangantawa da ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai da ayyukansu.