Gwamnatin jihar Kwara da ke arewa ta Tsakiyar Najeriya ta tabbatar da sako mutanen da aka yi garkuwa da su a yukan Woro da Nuku da ke ƙaramar hukumar Kiama bayan wata shida a hannun ƴanbindigar.
A watan Fabrairin wannan shekarar ne dai wasu ƴanbindiga suka kai hari ƙauyukan biyu tare da kashe fiye da mutum 75 da sace aƙalla mutum 175.
Cikin wata sanarwa da gwmanatin jihar ta fitar da tabbatar da sakin mutanen, sai dai ba ta yi ƙarin haske kan adadin wadanda aka sako ɗin ba.
Haka kuma sanarwar ba ta fayyace ko an biya kuɗin fansa kafin sakin mutanen ba.
Wani ɗan majalisar wakilai na yankin ya shaida wa BBC cewa yanzu haka mutanen da aka sako na hannun jami'an tsaro, inda suke samun kulawar likitoci, kafin sada su da iyalansu.
Harin da aka kai cikin watan Fabrairu lokacin sace mutanen, ya kasance ɗaya daga cikin munanan hare-haren da aka fi samun asarar rayuka a yankin cikin shekarun baya-bayan nan.
Hukumomi sun ɗora alhakin harin kan mayaƙa masu iƙirarin jihadi da ke cikin dazukan kusa da iyakar Najeriya da Benin.
Sakin mutanen ya zo ne makonni bayan sakin ɗalibai da malamai 44 da aka yi garkuwa da su a jihar Oyo, bayan sun shafe sama da makonni bakwai a hannun masu garkuwa da mutanen.
Najeriya na cewa tana kara ƙaimi wajen hare-haren soji kan ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai, amma har yanzu ƙasar fuskantar ƙalubalen tsaro da dama, da suka haɗa da hare-haren masu iƙirarin jihadi da garkuwa da mutane masu yawa.