KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 12/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 12 ga watan Agustan 2026.

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • Kano
  • Seriki Abbas
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman MINJIBIR

  1. Za mu farmaki cibiyoyin Amurka da na ƙawayenta idan aka sake kai mana hari - Iran

    ....

    Asalin hoton, Tasnim news agency

    Jami'in dakarun juyin juya halin Iran (IRGC), Hossein Mohebi, ya ce Amurka da ƙawayenta za su fuskanci hare-hare kan muhimman cibiyoyinsu idan aka sake kai wa Iran hari.

    Ya yi gargaɗin cewa Iran za ta iya kai farmaki kan tashoshin samar da wutar lantarki, layukan isar da makamashi da sauran muhimman tsare-tsaren Amurka da na ƙawayenta.

    Mohebi ya kuma ce, manyan sassan cibiyoyin sadarwa na duniya da ke da alaƙa da intanet na iya fuskantar barazana idan aka sake kai wa Iran hari.

    Ya ƙara da cewa a halin yanzu babu wani jirgin ruwa na Amurka da ke cikin ruwan Tekun Fasha.

    Kalaman kakakin IRGC na zuwa ne sa'o'i kaɗan bayan shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba yarda da Iran domin, a cewarsa, tana yi masa ƙarya.

    Trump ya kuma jaddada cewa Mashigin Hormuz yana ƙarƙashin ikon Amurka kuma mallakin Amurka ne.

  2. Assalamu alaikum

    Barka da zuwa shafin BBC Hausa na kai-tsaye.

    Kamar kullum, yau ma za mu muku labaran abubuwan da ke faruwa game da yaƙin Iran da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a wannan rana ta Laraba.

    Aisha Babangida ce za ta saka kasancewa da ku daga yanzu zuwa ƙarfe 4 na yamma.

    Za ku iya yin tsokaci a shafukanmu na sada zumunta: Facebook, X, instagram, YouTube da kuma zaurenmu na WhatssApp.

    Ku kasance da mu.