Za mu farmaki cibiyoyin Amurka da na ƙawayenta idan aka sake kai mana hari - Iran

Asalin hoton, Tasnim news agency
Jami'in dakarun juyin juya halin Iran (IRGC), Hossein Mohebi, ya ce Amurka da ƙawayenta za su fuskanci hare-hare kan muhimman cibiyoyinsu idan aka sake kai wa Iran hari.
Ya yi gargaɗin cewa Iran za ta iya kai farmaki kan tashoshin samar da wutar lantarki, layukan isar da makamashi da sauran muhimman tsare-tsaren Amurka da na ƙawayenta.
Mohebi ya kuma ce, manyan sassan cibiyoyin sadarwa na duniya da ke da alaƙa da intanet na iya fuskantar barazana idan aka sake kai wa Iran hari.
Ya ƙara da cewa a halin yanzu babu wani jirgin ruwa na Amurka da ke cikin ruwan Tekun Fasha.
Kalaman kakakin IRGC na zuwa ne sa'o'i kaɗan bayan shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba yarda da Iran domin, a cewarsa, tana yi masa ƙarya.
Trump ya kuma jaddada cewa Mashigin Hormuz yana ƙarƙashin ikon Amurka kuma mallakin Amurka ne.















