Abin da ya sa hukumar tace fina-finan Kano ta dakatar da jarumanta biyu
Hukumar tace fina-finan Kano ta yi ƙarin haske da dalilan da ya sa ta dakatar da wasu jarumanta biyu har na tsawo shekara guda.
Da safiya yau ne hukumar ta sanar da dakatar da Adam Garba da aka fi sani da Raba-gardama da kuma Amina Uba Hassan da ka fi sani da Jamila a cikin Labarina.
Cikin wata sanarwa da jami'in hulɗa da jama'a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan ganinsu a wani bidiyo da ta yi zargin ya saɓa wa tarbiya.
''An ɗauki matakin ne domin tabbatar da tsaftace tarbiya da nuna kyawawan ɗabi’u a dukkan bidiyoyin da ake fitarwa, tare da tabbatar da bin dokokin hukuma ya kamata'', in ji sanarwar.
Hukumar ta ce bidiyon ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’ummar Jihar Kano.
Sanarwar ta ci gaba da cewa dakatarwar na nufin an hana su gudanar da duk wani aikin fim a Jihar Kano har tsawon shekara guda.
''Karya wannan doka na iya jawo hukunci mai tsauri kamar yadda yake ƙunshe cikin tanadin dokar da ta kafa hukumar'', kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Sanarwar ta kuma ambato shugaban hukumar, Abba El-Mustapha na kira ga daraktoci da masu shirya fina-finai su mutunta wannan umarnin dakatarwa.
A nasa ɓangare jarumi Adam Garba ya nuna damuwarsa kan dakatarwar.
Cikin wata hira da kafar yaɗa labarai ta DCL Hausa ya ce ya kamata hukumar ta tuntuɓe su, domin jin abin da ya faru a bidiyon.