NDLEA ta kama ƴar Afirka Ta Kudu da hodar iblis a filin jirgin Abuja
Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) ta kama wata ’yar ƙasar Afirka ta Kudu mai shekara 38 a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja bayan gano kilo 5.75 na hodar iblis da aka ɓoye a cikin kayanta.
Hukumar ta ce matar ta yi ƙoƙarin amfani da ɗanta mai shekara uku a matsayin kariya don kauce wa cikakken binciken jami’an tsaro.
An kama ta ne bayan isowarta daga Doha a ƙasar Qatar.
NDLEA ta bayyana cewa da farko matar ta musanta mallakar jakunkunan da aka kama da hodar, amma bincike ya nuna alamun kayanta sun yi daidai da bayanan da ke fasfot ɗinta.
Daga bisani ta amsa cewa kayanta ne, bayan ta yi iƙirarin cewa ta manta ta yi rajistarsu.
A wani samame na daban, NDLEA ta kama wani ɗan Najeriya a filin jirgin saman Legas da ƙwayar methamphetamine, sannan ta ƙwace tabar wiwi mai nauyin kilo 4,143.5 da aka shigo da ita daga Canada, wadda darajarta ta haura naira biliyan 10.3.