Sakataren Majalisar Koli ta Tsaron ta Iran, Mohsen Rezaei, ya ce Iran ta fara amfani da wani makami mai linzami da ta ƙera da kanta domin tunkarar jiragen ruwan yaƙi na Amurka.
A wata hira da ya yi ta talabijin, Rezaei ya ce "Cikin sa'o'i 48 da suka gabata, mun gwada a karon farko wani makami mai linzami na Iran da aka ƙera domin yaƙar jiragen ruwan yaƙi. Wani jirgin ruwan Amurka ya kai masa hari, amma wannan makamin ya jefa Amurka cikin damuwa, har ta kai ga tilasta musu janyewa."
Sai dai rundunar sojin Amurka mai kula da yankin Gabas ta Tsakiya (CENTCOM) ba ta mayar da martani kai tsaye kan wannan iƙirari na Iran ba.
Amma a wata sanarwa da rundunar ta wallafa a dandalin X a jiya lahadi, wadda ake ganin tana nuni da wani hari da aka kai wa jiragen ruwanta biyu, ta ce "saƙonmu ga dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran a bayyane yake''.
''Idan kuka kai hari kan jiragen ruwanmu biyu, za mu ƙaƙaba ƙarin tsauraran takunkuman tattalin arziki kuma mu lalata uku daga cikin jiragen ruwanku."
Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen kare dakarunta ba.
''Kuma idan ya zama dole, za mu lalata wasu daga cikin tankokin dakon man fetur na Iran idan suka tsinci kansu a cikin yanayi mai rauni."
Mohsen Rezaei, wanda tsohon kwamandan dakarun juyin juya halin Iran ne, ya kuma yi magana kan irin ƙalubalen da jiragen ruwa masu dakon kaya da ke aiki a yankin za su iya fuskanta.
"Duk wani jirgin ruwa da ya karya sharuɗɗan da aka gindaya, kuma ya yi aiki a yankin ba tare da tuntuɓar Iran ba, za a sanya shi cikin jerin takunkuman Iran. Haka kuma zai iya fuskantar wasu matsaloli, ciki har da wahalar zirga-zirga a yankin nan gaba."