Mayaƙan Houthi sun sake kai hare-hare kan cibiyoyin soji a Saudiyya
Ƴan tawayen Houthi na Yemen sun sake kai hare-hare kan cibiyoyin soja a Saudiyya ta amfani da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa a ranar Litinin.
Houthi sun ce sun harba jirage marasa matuƙa da kuma makamai masu linzami da dama zuwa cikin ƙasar Saudiyya.
Bayan hare-haren, hukumomin kare fararen hula na Saudiyya sun fitar da gajeren gargaɗi ga mazauna biranen Khamis Mushait da Abha, waɗanda ke kusa da iyakar Yemen.
A baya-bayan nan ne Houthi suka ƙwace iko da gaɓar Tekun Maliya da kuma mashigar ruwan Bab al-Mandab.
Muhimmancin wannan hanyar ruwa ya ƙaru sakamakon matsalolin da suka addabi zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz a lokacin yaƙin Amurka da Iran.
Wani mazaunin birnin Khamis Mushait a Saudiyya ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa ya ji "manyan ƙarar fashe-fashe" waɗanda suka haddasa gobara da ta ci gaba da ƙonewa "na dogon lokaci".
"Ko kaɗan ba mu samu damar yin barci ba," in ji shi.