Atiku ya taya Adeleke murnar sake lashe zaɓen gwamnan Osun
Tsohon mataimakin shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC a zaɓen 2027, Atiku Abubakar, ya taya Ademola Adeleke murnar nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan jihar Osun.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Lahadi, Atiku ya ce nasarar Adeleke ta nuna ƙarara zaɓin al'ummar jihar Osun, wanda suka bayyana ta hanyar ƙuri'un da suka kaɗa a zaɓen.
Ya kuma yaba wa al'ummar jihar kan yadda suka fito cikin lumana tare da nuna himma wajen gudanar da zaɓen.
Atiku ya ce yana yi wa Adeleke fatan samun ƙarin nasara yayin da yake ci gaba da yi wa mutanen Osun hidima a matsayinsa na gwamna.