Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 16/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Lahadi 16 ga watan Agustan 2026

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammed

  1. Atiku ya taya Adeleke murnar sake lashe zaɓen gwamnan Osun

    Tsohon mataimakin shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC a zaɓen 2027, Atiku Abubakar, ya taya Ademola Adeleke murnar nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan jihar Osun.

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Lahadi, Atiku ya ce nasarar Adeleke ta nuna ƙarara zaɓin al'ummar jihar Osun, wanda suka bayyana ta hanyar ƙuri'un da suka kaɗa a zaɓen.

    Ya kuma yaba wa al'ummar jihar kan yadda suka fito cikin lumana tare da nuna himma wajen gudanar da zaɓen.

    Atiku ya ce yana yi wa Adeleke fatan samun ƙarin nasara yayin da yake ci gaba da yi wa mutanen Osun hidima a matsayinsa na gwamna.

  2. Mun kama wanda ake zargi da harbi a wajen biki a Kano - Ƴansanda

    Rundunar ’yansandan Kano ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da harbin mutane a wajen bikin aure a Tudun Yola Bajallabe.

    A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin sada zumuntarta na X, ta ce jami’anta sun gaggauta isa wurin bayan samun kiran neman agaji, inda suka kama wanda ake zargin tare da kwacd bindigar da aka yi amfani da ita wajen harbin.

    Ta ƙara da cewa an garzaya da mutane huɗu da suka jikkata zuwa sakamakon harbin zuwa asibiti domin samun magani, sai dai likita ya tabbatar da mutuwar ɗaya daga cikinsu.

    Rundunar ta ce sashen binciken manyan laifuka na SCID da ke Bompai na ci gaba da binciken lamarin.

  3. Yadda Davido ya yi murnar sanar da kawunsa ya lashe zaɓen gwamnan Osun

    Ga wani bidiyo da ke nuna yadda shahararren mawaƙin Najeriya, Davido, ya yi murnar nasarar kawunsa, Ademola Adeleke, bayan da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Osun.

    An ga mawaƙin cikin farin ciki yayin da yake shagulgulan nasarar tare da waɗanda ke tare da shi.

    Bidiyon, wanda Davido ya wallafa a shafinsa na X, ya nuna yadda mawaƙin da wasu mutane ke murna da raye-raye bayan sanar da sakamakon zaɓen.

    A sakamakon da INEC ta sanar, Adeleke ya samu ƙuri'u 511,067 inda ya kayar da babban abokin hamayyarsa, Bola Oyebamiji na jam'iyyar APC, wanda ya samu ƙuri'u 444,815. Sakamakon ya tabbatar da ci gaba da zamansa gwamnan jihar Osun.

    Faifan bidiyon ya yi ta samun martani a kafafen sada zumunta, inda magoya baya da sauran masu amfani da shafukan intanet suka rika taya Davido da kawunsa murnar wannan nasara a zaɓen gwamnan jihar.

  4. Iran ta nemi Qatar ta ba ta damar binciken batun matukan jiragenta da ke tsare a ƙasar

    Iran ta nemi Qatar ta ba ƙwararrun rundunar sojin saman ƙasarta damar shiga ƙasar domin gudanar da bincike kan makomar matukan jiragenta uku da ta ce ana tsare da su.

    Kwamandan kwamitin neman mutanen da suka ɓace na rundunar sojin Iran, Mohammad Bagherzadeh, ya ce ƙwararrun Iran sun shafe watanni suna jiran izinin shiga Qatar, yana zargin hukumomin Qatar da jinkirta binciken.

    Ya kuma buƙaci Red Cross ta gaggauta bibiyar lamarin, tare da bayyana damuwa kan wasu ƴan Iran huɗu da ya ce ana tsare da su a Kuwait.

    Qatar ta musanta cewa tana tsare da matukan jiragen uku. Kakakin ma'aikatar harkokin wajen ƙasar, Majid Ansari, ya ce matuƙan sun shiga sararin samaniyar Qatar a watan Maris, kuma Qatar ta ɗauki matakin kare ƙasarta bisa dokokin kasa da kasa.

  5. INEC ta ayyana Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Osun

    Hukumar zaɓe ta ƙasa mai zaman kanta (INEC) ta ayyana gwamnan jihar Osun mai ci, Ademola Adeleke, a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna da aka gudanar a ranar 14 ga watan Agusta.

    A sakamakon da hukumar ta bayyana, Adeleke na jam'iyyar Accord ya samu ƙuri'u 511,067, inda ya kayar da babban abokin hamayyarsa Bola Oyebamiji na jam'iyyar APC, wanda ya samu ƙuri'u 444,815. Hakazalika, ɗan takarar jam'iyyar ADC, Najeem Salaam, ya zo na uku bayan samun ƙuri'u 17,180.

    Sakamakon zaɓen daga ƙananan hukumomi daban-daban na jihar ya nuna cewa Adeleke ya yi nasara a mafi yawan yankunan da aka kaɗa ƙuri'a, lamarin da ya taimaka masa wajen samun gagarumar rinjaye da kuma ci gaba da zama gwamnan jihar Osun na wani wa'adi.

  6. Iran ta gargaɗi Trump ya damu da tsaron kansa maimakon mashigar Hormuz

    Shugaban Kwamitin Tsaro da Harkokin Waje na Majalisar Iran, Ebrahim Azizi, ya mayar da martani ga kalaman Donald Trump kan mashigar Hormuz, yana mai cewa shugaban na Amurka ya kamata ya damu da tsaronsa maimakon ci gaba da yin barazana game da mashigin ruwan.

    Kalaman na sa sun zo ne a matsayin martani ga abin da Donald Trump ya faɗa a jiya inda ya ce zai ayyana mashigar Hormuz a matsayin na Amurka.

    Daga baya fadar White House ta ce kalaman Trump shaci faɗi ce amma kalaman nasa sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen yaɗa labarai da kuma tsakanin jami'an gwamnati da 'yan siyasar Iran.

    Mashigar Hormuz na daga cikin muhimman hanyoyin jigilar man fetur a duniya, lamarin da ke sa duk wata magana a kansa ta ja hankalin ƙasashen duniya..

  7. Sabon shugaban Hamas ya isa Alkahira domin tattaunawa kan Gaza

    Sabon shugaban ungiyar Hamas Khalil al-Hayyah, ya isa birnin Alkahira na Masar domin tattaunawa da jami'an ƙasar kan halin da ake ciki a Gaza, a cewar majiyoyin Hamas.

    Tashar Al Jazeera ta ruwaito cewa ana sa ran al-Hayyah zai gana da Hassan Rashad, shugaban hukumar leƙen asirin Masar, a safiyar Lahadi.

    Wannan ita ce ziyararsa ta farko zuwa Masar tun bayan da ya karɓi jagorancin Hamas a ƙarshen watan Yuli.

    Ziyarar tasa na zuwa ne gabanin wata tafiya da Jared Kushner, surukin shugaban Amurka Donald Trump, zai kai yankin.

    Ana sa ran Kushner zai ziyarci Isra'ila da Masar a mako mai zuwa domin ƙoƙarin rage saɓanin da ke akwai kan wani shiri da ya shafi Gaza, wanda Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi watsi da shi.

    Haka kuma, ana sa ran wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya mai kula da harkokin zaman lafiya a Gaza, Nickolay Mladenov, zai raka Kushner a wannan tafiya.

  8. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da Safiyar ranar Lahadi.

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.