Rundunar Sojin Najeriya ta cafke baƙin haure 24 a Legas
Rundunar sojin Najeriya ta ce ta kama wasu baƙin haure 24 da ba su da takardun zama a ƙasar.
A cikin wata sanarwa da mataimakin daraktan hulɗa da jama'a na rundunar ta 81, Laftanar Kanal Musa Yahaya ya fitar a ranar Alhamis, ya ce an kama mutanen ne a yayin wani a wani samame da ta kai a ƙaramar hukumar Epe da ke jihar Legas.
Ta ce ta kai samamen bayan bayanan sirri da suka nuna akwai wasu baƙin haure da ba su da takardun izini a yankin.
Sanarwar ta ce sojoji tare da haɗin gwiwar jami'an sa-kai ne suka kai samame wani gida a yankin Imokun da ke Odo-Noforija/Poka, inda suka kama mutum 24 - maza 15 da mata 9.
Binciken ya nuna cewa mutum 10 daga cikin waɗanda aka kama ƴan Kamaru ne, 6 daga Togo, uku-uku daga Côte d’Ivoire da Jamhuriyar Benin, sai ɗaya-ɗaya daga Burkina Faso da Guinea-Bissau.
Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike domin tantance matsayin shigowarsu Najeriya, dalilin zamansu da kuma ko suna da hannu a wasu ayyukan da suka saɓa wa doka.
Haka kuma, jami'ai na ƙoƙarin gano mai gidan da aka kama su a ciki domin yi masa tambayoyi kan yadda suka zauna a wurin da kuma irin ayyukan da suke gudanarwa.
Daga bisani an miƙa mutanen ga hukumar kula da shige da fice ta Najeriya reshen jihar Legas domin ci gaba da bincike da ɗaukar matakan da suka dace.